Ana SayfaMealler › M.Gumi
MG

M.Gumi

M.Gumi
M.Gumi meali ile okumaya başla
Abese 1 / 42
1
Yã game huska kuma ya jũya bãya.
M.Gumi 80:1
2
Sabõda makãho yã je masa.
M.Gumi 80:2
3
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
M.Gumi 80:3
4
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
M.Gumi 80:4
5
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
M.Gumi 80:5
6
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
M.Gumi 80:6
7
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
M.Gumi 80:7
8
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
M.Gumi 80:8
9
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
M.Gumi 80:9
10
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
M.Gumi 80:10
11
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
M.Gumi 80:11
12
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
M.Gumi 80:12
13
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
M.Gumi 80:13
14
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
M.Gumi 80:14
15
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
M.Gumi 80:15
16
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
M.Gumi 80:16
17
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
M.Gumi 80:17
18
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
M.Gumi 80:18
19
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
M.Gumi 80:19
20
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
M.Gumi 80:20
21
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
M.Gumi 80:21
22
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
M.Gumi 80:22
23
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
M.Gumi 80:23
24
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
M.Gumi 80:24
25
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
M.Gumi 80:25
26
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
M.Gumi 80:26
27
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
M.Gumi 80:27
28
Da inabi da ciyãwa.
M.Gumi 80:28
29
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
M.Gumi 80:29
30
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
M.Gumi 80:30