1
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
2
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
3
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
4
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
5
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
6
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri
7
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
8
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.
9
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya
10
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.
11
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,
12
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya
14
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
15
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!
16
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.
17
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
18
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)
19
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
20
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
21
Sa'an nan, ya yi tunãni
22
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
23
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
24
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
25
Wannan maganar mutum dai ce.
26
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
27
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
28
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.
29
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
30
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.
Sonraki 26 ayet →