Ana SayfaMealler › M.Gumi
MG

M.Gumi

M.Gumi
M.Gumi meali ile okumaya başla
Hakka 1 / 52
1
Kiran gaskiya!
M.Gumi 69:1
2
Mẽne ne kiran gaskiya?
M.Gumi 69:2
3
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
M.Gumi 69:3
4
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
M.Gumi 69:4
5
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
M.Gumi 69:5
6
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
M.Gumi 69:6
7
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
M.Gumi 69:7
8
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
M.Gumi 69:8
9
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
M.Gumi 69:9
10
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
M.Gumi 69:10
11
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
M.Gumi 69:11
12
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
M.Gumi 69:12
13
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
M.Gumi 69:13
14
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
M.Gumi 69:14
15
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
M.Gumi 69:15
16
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
M.Gumi 69:16
17
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
M.Gumi 69:17
18
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
M.Gumi 69:18
19
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
M.Gumi 69:19
20
Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne.
M.Gumi 69:20
21
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
M.Gumi 69:21
22
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
M.Gumi 69:22
23
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
M.Gumi 69:23
24
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
M.Gumi 69:24
25
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
M.Gumi 69:25
26
Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!
M.Gumi 69:26
27
In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
M.Gumi 69:27
28
Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!
M.Gumi 69:28
29
Ĩkona ya ɓace mini!
M.Gumi 69:29
30
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
M.Gumi 69:30