1
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
2
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
3
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
4
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
5
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
7
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
8
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
9
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
10
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
11
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
12
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
13
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
14
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
15
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
16
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
17
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
18
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
19
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
20
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
21
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
22
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
23
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
24
Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!
25
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
26
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
27
Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne.
28
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
29
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
30
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
Sonraki 22 ayet →