1
Idan mai aukuwa ta auku.
2
Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.
3
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
4
Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.
5
Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.
6
Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.
7
Kuma kun kasance nau'i uku.
8
Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
9
Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?
10
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
11
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
12
A ckin Aljannar ni'ima.
13
Jama'a ne daga mutãnen farko.
14
Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.
15
(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.
16
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
17
Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.
18
Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.
19
Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.
20
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
21
Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.
22
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
23
Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.
24
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
25
Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.
26
Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.
27
Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
28
(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.
29
Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.
30
Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.
Sonraki 30 ayet →