4
Yã sanar da shi bayãni (magana).
5
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
6
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
7
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
8
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
9
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
10
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
11
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
12
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
13
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
14
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
15
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
16
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
17
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
18
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
19
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
20
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
21
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
22
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
23
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
24
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
25
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
26
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.
27
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
28
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
29
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.
30
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
Sonraki 30 ayet →