Ana SayfaMealler › M.Gumi
MG

M.Gumi

M.Gumi
M.Gumi meali ile okumaya başla
Zariyat 1 / 60
1
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
M.Gumi 51:1
2
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
M.Gumi 51:2
3
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
M.Gumi 51:3
4
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
M.Gumi 51:4
5
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
M.Gumi 51:5
6
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
M.Gumi 51:6
7
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
M.Gumi 51:7
8
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
M.Gumi 51:8
9
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
M.Gumi 51:9
10
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
M.Gumi 51:10
11
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
M.Gumi 51:11
12
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
M.Gumi 51:12
13
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
M.Gumi 51:13
14
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
M.Gumi 51:14
15
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
M.Gumi 51:15
16
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
M.Gumi 51:16
17
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
M.Gumi 51:17
18
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
M.Gumi 51:18
19
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
M.Gumi 51:19
20
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
M.Gumi 51:20
21
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
M.Gumi 51:21
22
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
M.Gumi 51:22
23
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
M.Gumi 51:23
24
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
M.Gumi 51:24
25
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
M.Gumi 51:25
26
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
M.Gumi 51:26
27
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
M.Gumi 51:27
28
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
M.Gumi 51:28
29
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
M.Gumi 51:29
30
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
M.Gumi 51:30