Ana SayfaMealler › M.Gumi
MG

M.Gumi

M.Gumi
M.Gumi meali ile okumaya başla
Şuara 1 / 227
1
¦. S̃. M̃.
M.Gumi 26:1
2
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
M.Gumi 26:2
3
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
M.Gumi 26:3
4
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
M.Gumi 26:4
5
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
M.Gumi 26:5
6
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
M.Gumi 26:6
7
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
M.Gumi 26:7
8
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
M.Gumi 26:8
9
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
M.Gumi 26:9
10
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
M.Gumi 26:10
11
Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?
M.Gumi 26:11
12
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
M.Gumi 26:12
13
Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
M.Gumi 26:13
14
Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni.
M.Gumi 26:14
15
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
M.Gumi 26:15
16
Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne.
M.Gumi 26:16
17
Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu.
M.Gumi 26:17
18
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
M.Gumi 26:18
19
Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?
M.Gumi 26:19
20
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
M.Gumi 26:20
21
Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni.
M.Gumi 26:21
22
Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla.
M.Gumi 26:22
23
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
M.Gumi 26:23
24
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
M.Gumi 26:24
25
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
M.Gumi 26:25
26
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
M.Gumi 26:26
27
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
M.Gumi 26:27
28
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
M.Gumi 26:28
29
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
M.Gumi 26:29
30
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
M.Gumi 26:30