Ana SayfaMealler › M.Gumi
MG

M.Gumi

M.Gumi
M.Gumi meali ile okumaya başla
Hicr 1 / 99
1
A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
M.Gumi 15:1
2
Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
M.Gumi 15:2
3
Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
M.Gumi 15:3
4
Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
M.Gumi 15:4
5
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
M.Gumi 15:5
6
Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
M.Gumi 15:6
7
Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?
M.Gumi 15:7
8
Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
M.Gumi 15:8
9
Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
M.Gumi 15:9
10
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
M.Gumi 15:10
11
Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
M.Gumi 15:11
12
Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
M.Gumi 15:12
13
Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
M.Gumi 15:13
14
Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
M.Gumi 15:14
15
Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
M.Gumi 15:15
16
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
M.Gumi 15:16
17
Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
M.Gumi 15:17
18
Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
M.Gumi 15:18
19
Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
M.Gumi 15:19
20
Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
M.Gumi 15:20
21
Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
M.Gumi 15:21
22
Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
M.Gumi 15:22
23
Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
M.Gumi 15:23
24
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
M.Gumi 15:24
25
Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
M.Gumi 15:25
26
Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
M.Gumi 15:26
27
Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
M.Gumi 15:27
28
Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
M.Gumi 15:28
29
To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada.
M.Gumi 15:29
30
Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
M.Gumi 15:30