1
Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?
2
Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?
3
Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.
4
Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.
5
Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?